الإنفطار · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 587 na Alkur'ani

Shafi 587 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 25. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 587 dans le Coran

25
ayoyi
30
Juz
59
Hizb
2
Surah
Juz 30
Shafi 587
سورة الإنفطار
Juz 30 27.8% (157/564)
Hizb 59 56.9% (157/276)

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتْ ﴿١﴾

Idan sama ta tsãge.

وَإِذَا ٱلْكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتْ ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka wãtse.

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ فُجِّرَتْ ﴿٣﴾

Kuma idan tẽkuna aka facce su.

وَإِذَا ٱلْقُبُورُ بُعْثِرَتْ ﴿٤﴾

Kuma idan kaburbura aka tõne su.

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ ﴿٥﴾

Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلْكَرِيمِ ﴿٦﴾

Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

ٱلَّذِى خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ ﴿٧﴾

Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.

فِىٓ أَىِّ صُورَةٍۢ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ ﴿٨﴾

A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.

كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ ﴿٩﴾

A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!

وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَـٰفِظِينَ ﴿١٠﴾

Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.

كِرَامًۭا كَـٰتِبِينَ ﴿١١﴾

Mãsu daraja, marubũta.

يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ ﴿١٢﴾

Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.

إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍۢ ﴿١٣﴾

Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.

وَإِنَّ ٱلْفُجَّارَ لَفِى جَحِيمٍۢ ﴿١٤﴾

Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.

يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ ٱلدِّينِ ﴿١٥﴾

Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.

وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَآئِبِينَ ﴿١٦﴾

Bã zã su faku daga gare ta ba.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ ﴿١٧﴾

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?

ثُمَّ مَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ ﴿١٨﴾

Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?

يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌۭ لِّنَفْسٍۢ شَيْـًۭٔا ۖ وَٱلْأَمْرُ يَوْمَئِذٍۢ لِّلَّهِ ﴿١٩﴾

Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.

وَيْلٌۭ لِّلْمُطَفِّفِينَ ﴿١﴾

Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.

ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكْتَالُوا۟ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسْتَوْفُونَ ﴿٢﴾

Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.

وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ ﴿٣﴾

Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa

أَلَا يَظُنُّ أُو۟لَـٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ ﴿٤﴾

Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?

لِيَوْمٍ عَظِيمٍۢ ﴿٥﴾

Domin yini mai girma.

يَوْمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٦﴾

Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah