Kara Shafi 599 na Alkur'ani

Shafi 599 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 18. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Shafi 599 a cikin Alkur'ani

18
ayoyi
30
Juz
60
Hizb
3
Surah
البينة · Juz 30
Juz 30
Shafi 599
سورة البينة
Juz 30 82.4% (465/564)
Hizb 60 65.6% (189/288)

جَزَآؤُهُمْ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّـٰتُ عَدْنٍۢ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَـٰرُ خَـٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًۭا ۖ رَّضِىَ ٱللَّهُ عَنْهُمْ وَرَضُوا۟ عَنْهُ ۚ ذَٰلِكَ لِمَنْ خَشِىَ رَبَّهُۥ ﴿٨﴾

Sakamakonsu, a wurin Ubangijinsu, shi ne gidajen Aljannar zama, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu sunã madawwama a cikinta har abada. Allah Ya yarda da su, kuma su, sun yarda da Shi. wannan sakamako ne ga wanda ya ji tsõron Ubangijinsa.

إِذَا زُلْزِلَتِ ٱلْأَرْضُ زِلْزَالَهَا ﴿١﴾

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

وَأَخْرَجَتِ ٱلْأَرْضُ أَثْقَالَهَا ﴿٢﴾

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

وَقَالَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا لَهَا ﴿٣﴾

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

يَوْمَئِذٍۢ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا ﴿٤﴾

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا ﴿٥﴾

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

يَوْمَئِذٍۢ يَصْدُرُ ٱلنَّاسُ أَشْتَاتًۭا لِّيُرَوْا۟ أَعْمَـٰلَهُمْ ﴿٦﴾

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًۭا يَرَهُۥ ﴿٧﴾

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍۢ شَرًّۭا يَرَهُۥ ﴿٨﴾

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.

وَٱلْعَـٰدِيَـٰتِ ضَبْحًۭا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.

فَٱلْمُورِيَـٰتِ قَدْحًۭا ﴿٢﴾

Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.

فَٱلْمُغِيرَٰتِ صُبْحًۭا ﴿٣﴾

Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.

فَأَثَرْنَ بِهِۦ نَقْعًۭا ﴿٤﴾

Sai su motsar da ƙũra game da shi.

فَوَسَطْنَ بِهِۦ جَمْعًا ﴿٥﴾

Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.

إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٌۭ ﴿٦﴾

Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.

وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٌۭ ﴿٧﴾

Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka.

وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلْخَيْرِ لَشَدِيدٌ ﴿٨﴾

Kuma 1alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.

۞ أَفَلَا يَعْلَمُ إِذَا بُعْثِرَ مَا فِى ٱلْقُبُورِ ﴿٩﴾

Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.

بسم الله الرحمن الرحيم Lar 20 Safar
الأربعاء 20 صفر
أحدب متناقص Cikakken Wata Raguwa Rana 21.9 / 29.5
Haske 53%
Wata Sabo a cikin kwana 8
أستغفر الله Ina neman gafara daga Allah