Kara Surah At-Takwir

Surah At-Takwir (التكوير) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 29. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

📖 Karatu minti 1

Surah At-Takwir cikin lambobi

Tsarin saukarwa
Saukarwa n° 7 / 114
(na Makka)
104
kalmomi
-85.5% vs matsakaici
449
haruffa
-85.4% vs matsakaici
1
min karantawa
29
ayoyi
-47.0% vs matsakaici

Yawan amfani da kalmomin bincike

الله 1
رب 1

Haruffa da yawa suke fitowa

ل
45
#1
و
36
#2
ا
33
#3
ن
30
#4
م
27
#5
التكوير · Juz 30
Kara Surah At-Takwir
سورة التكوير
Juz 30 22.7% (128/564)
Hizb 59 46.4% (128/276)

إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ ﴿١﴾

Idan rãna aka shafe haskenta

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ ﴿٣﴾

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ ﴿٤﴾

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ ﴿٥﴾

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ ﴿٦﴾

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ ﴿٧﴾

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ ﴿٨﴾

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

بِأَىِّ ذَنۢبٍۢ قُتِلَتْ ﴿٩﴾

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ ﴿١٠﴾

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ ﴿١١﴾

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ ﴿١٢﴾

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ ﴿١٣﴾

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّآ أَحْضَرَتْ ﴿١٤﴾

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ ﴿١٥﴾

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ ﴿١٦﴾

Mãsu gudu suna ɓũya.

وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ ﴿١٧﴾

Da dare idan ya bãyar da bãya.

وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ ﴿١٨﴾

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ ﴿١٩﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍۢ ﴿٢٠﴾

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

مُّطَاعٍۢ ثَمَّ أَمِينٍۢ ﴿٢١﴾

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍۢ ﴿٢٢﴾

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ ﴿٢٣﴾

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍۢ ﴿٢٤﴾

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍۢ رَّجِيمٍۢ ﴿٢٥﴾

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ ﴿٢٦﴾

Shin, a inã zã ku tafi?

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَـٰلَمِينَ ﴿٢٧﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ ﴿٢٨﴾

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٢٩﴾

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

بسم الله الرحمن الرحيم Lit 10 Rabi' al-Awwal
الاثنين 10 ربيع الأول
أحدب متزايد Cikakken Wata Tasowa Rana 11.6 / 29.5
Haske 89%
Cikakken Wata a cikin kwana 3
أستغفر الله Ina neman gafara daga Allah