الأعلى · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Hizb 60 na Alkur'ani

Hizb 60 wani ɓangare ne na Juz 30. Yana ɗauke da ayoyi 288 a shafi(shafuffuka) 13 na Mushaf.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Shafi 592
Hizb 60
سورة الأعلى
Juz 30 51.6% (291/564)
Hizb 60 5.2% (15/288)

بَلْ تُؤْثِرُونَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا ﴿١٦﴾

Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.

وَٱلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌۭ وَأَبْقَىٰٓ ﴿١٧﴾

Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

إِنَّ هَـٰذَا لَفِى ٱلصُّحُفِ ٱلْأُولَىٰ ﴿١٨﴾

Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farko.

صُحُفِ إِبْرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ ﴿١٩﴾

Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْغَـٰشِيَةِ ﴿١﴾

Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ خَـٰشِعَةٌ ﴿٢﴾

Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.

عَامِلَةٌۭ نَّاصِبَةٌۭ ﴿٣﴾

Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.

تَصْلَىٰ نَارًا حَامِيَةًۭ ﴿٤﴾

Zã su shiga wata wuta mai zãfi.

تُسْقَىٰ مِنْ عَيْنٍ ءَانِيَةٍۢ ﴿٥﴾

Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.

لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍۢ ﴿٦﴾

Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.

لَّا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِى مِن جُوعٍۢ ﴿٧﴾

Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاعِمَةٌۭ ﴿٨﴾

Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.

لِّسَعْيِهَا رَاضِيَةٌۭ ﴿٩﴾

Game da aikinsu, masu yarda ne.

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ ﴿١٠﴾

(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.

لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَـٰغِيَةًۭ ﴿١١﴾

Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.

فِيهَا عَيْنٌۭ جَارِيَةٌۭ ﴿١٢﴾

A cikinta akwai marmaro mai gudãna.

فِيهَا سُرُرٌۭ مَّرْفُوعَةٌۭ ﴿١٣﴾

A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.

وَأَكْوَابٌۭ مَّوْضُوعَةٌۭ ﴿١٤﴾

Da kõfuna ar'aje.

وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌۭ ﴿١٥﴾

Da filõli jẽre,

وَزَرَابِىُّ مَبْثُوثَةٌ ﴿١٦﴾

Da katifu shimfiɗe.

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ ﴿١٧﴾

Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيْفَ رُفِعَتْ ﴿١٨﴾

Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?

وَإِلَى ٱلْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ ﴿١٩﴾

Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?

وَإِلَى ٱلْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ ﴿٢٠﴾

Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?

فَذَكِّرْ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٌۭ ﴿٢١﴾

sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ ﴿٢٢﴾

Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ ﴿٢٣﴾

Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَكْبَرَ ﴿٢٤﴾

To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.

إِنَّ إِلَيْنَآ إِيَابَهُمْ ﴿٢٥﴾

Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُم ﴿٢٦﴾

Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.

Shafi 593
Hizb 60
سورة الفجر
Juz 30 56.9% (321/564)
Hizb 60 15.6% (45/288)

وَٱلْفَجْرِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da alfijiri.

وَلَيَالٍ عَشْرٍۢ ﴿٢﴾

Da darũruwa gõma.

وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ ﴿٣﴾

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ ﴿٤﴾

Da dare idan yana shũɗewa.

هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌۭ لِّذِى حِجْرٍ ﴿٥﴾

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ ﴿٦﴾

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ ﴿٧﴾

Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ ﴿٨﴾

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ ﴿٩﴾

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ ﴿١٠﴾

Da Fir'auna mai turãku.

ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ ﴿١١﴾

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ ﴿١٢﴾

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ ﴿١٣﴾

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ ﴿١٤﴾

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ ﴿١٥﴾

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ ﴿١٦﴾

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ ﴿١٧﴾

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ ﴿١٨﴾

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًۭا لَّمًّۭا ﴿١٩﴾

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّۭا جَمًّۭا ﴿٢٠﴾

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّۭا دَكًّۭا ﴿٢١﴾

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّۭا صَفًّۭا ﴿٢٢﴾

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍۢ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ ﴿٢٣﴾

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

Shafi 594
Hizb 60
سورة الفجر
Juz 30 61.0% (344/564)
Hizb 60 23.6% (68/288)

يَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى ﴿٢٤﴾

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌۭ ﴿٢٥﴾

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌۭ ﴿٢٦﴾

Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ ﴿٢٧﴾

Yã kai rai mai natsuwa!

ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةًۭ مَّرْضِيَّةًۭ ﴿٢٨﴾

Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

فَٱدْخُلِى فِى عِبَـٰدِى ﴿٢٩﴾

Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

وَٱدْخُلِى جَنَّتِى ﴿٣٠﴾

Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).

لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ﴿١﴾

Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ﴿٢﴾

Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

وَوَالِدٍۢ وَمَا وَلَدَ ﴿٣﴾

Da mahaifi da abin da ya haifa.

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِى كَبَدٍ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌۭ ﴿٥﴾

Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًۭا لُّبَدًا ﴿٦﴾

Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ ﴿٧﴾

Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ ﴿٨﴾

Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

وَلِسَانًۭا وَشَفَتَيْنِ ﴿٩﴾

Da harshe, da leɓɓa biyu.

وَهَدَيْنَـٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ ﴿١٠﴾

Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ ﴿١١﴾

To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ ﴿١٢﴾

Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

فَكُّ رَقَبَةٍ ﴿١٣﴾

Ita ce fansar wuyan bãwa.

أَوْ إِطْعَـٰمٌۭ فِى يَوْمٍۢ ذِى مَسْغَبَةٍۢ ﴿١٤﴾

Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

يَتِيمًۭا ذَا مَقْرَبَةٍ ﴿١٥﴾

Ga marãya ma'abũcin zumunta.

أَوْ مِسْكِينًۭا ذَا مَتْرَبَةٍۢ ﴿١٦﴾

Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ ﴿١٧﴾

Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

أُو۟لَـٰٓئِكَ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ ﴿١٨﴾

Waɗannan ne ma'abũta albarka

وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا هُمْ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ ﴿١٩﴾

Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

عَلَيْهِمْ نَارٌۭ مُّؤْصَدَةٌۢ ﴿٢٠﴾

A kansu akwai wata wuta abar kullewa.

Shafi 595
Hizb 60
سورة الشمس
Juz 30 65.8% (371/564)
Hizb 60 33.0% (95/288)

وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.

وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا ﴿٢﴾

Kuma da wata idan ya bi ta.

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا ﴿٣﴾

Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا ﴿٤﴾

Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا ﴿٥﴾

Da sama da abin da ya gina ta.

وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا ﴿٦﴾

Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.

وَنَفْسٍۢ وَمَا سَوَّىٰهَا ﴿٧﴾

Da rai da abin da ya daidaita shi.

فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا ﴿٨﴾

Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.

قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا ﴿٩﴾

Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.

وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا ﴿١٠﴾

Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ ﴿١١﴾

Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا ﴿١٢﴾

A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).

فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَـٰهَا ﴿١٣﴾

Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا ﴿١٤﴾

Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).

وَلَا يَخَافُ عُقْبَـٰهَا ﴿١٥﴾

Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.

وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ ﴿٢﴾

Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.

وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ ﴿٣﴾

Da abin da ya halitta namiji da mace.

إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ ﴿٤﴾

Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.

فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ ﴿٥﴾

To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.

وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ ﴿٦﴾

Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ ﴿٧﴾

To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.

وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ ﴿٨﴾

Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.

وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ ﴿٩﴾

Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ ﴿١٠﴾

To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.

وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ ﴿١١﴾

Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).

إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ ﴿١٢﴾

Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.

وَإِنَّ لَنَا لَلْـَٔاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ ﴿١٣﴾

Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.

فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًۭا تَلَظَّىٰ ﴿١٤﴾

Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.

Shafi 596
Hizb 60
سورة الليل
Juz 30 70.9% (400/564)
Hizb 60 43.1% (124/288)

لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى ﴿١٥﴾

Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.

ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ ﴿١٦﴾

Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.

وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى ﴿١٧﴾

Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.

ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾

Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍۢ تُجْزَىٰٓ ﴿١٩﴾

Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.

إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٠﴾

Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.

وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ ﴿٢١﴾

To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).

وَٱلضُّحَىٰ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da hantsi.

وَٱلَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ ﴿٢﴾

Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ ﴿٣﴾

Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.

وَلَلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌۭ لَّكَ مِنَ ٱلْأُولَىٰ ﴿٤﴾

Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.

وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰٓ ﴿٥﴾

Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.

أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًۭا فَـَٔاوَىٰ ﴿٦﴾

Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?

وَوَجَدَكَ ضَآلًّۭا فَهَدَىٰ ﴿٧﴾

Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?

وَوَجَدَكَ عَآئِلًۭا فَأَغْنَىٰ ﴿٨﴾

Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?

فَأَمَّا ٱلْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ ﴿٩﴾

Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.

وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنْهَرْ ﴿١٠﴾

Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.

وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ ﴿١١﴾

Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).

أَلَمْ نَشْرَحْ لَكَ صَدْرَكَ ﴿١﴾

Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?

وَوَضَعْنَا عَنكَ وِزْرَكَ ﴿٢﴾

Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.

ٱلَّذِىٓ أَنقَضَ ظَهْرَكَ ﴿٣﴾

Wanda ya nauyayi bãyanka?

وَرَفَعْنَا لَكَ ذِكْرَكَ ﴿٤﴾

Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?

فَإِنَّ مَعَ ٱلْعُسْرِ يُسْرًا ﴿٥﴾

To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.

إِنَّ مَعَ ٱلْعُسْرِ يُسْرًۭا ﴿٦﴾

Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.

فَإِذَا فَرَغْتَ فَٱنصَبْ ﴿٧﴾

Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرْغَب ﴿٨﴾

Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.

Shafi 597
Hizb 60
سورة التين
Juz 30 75.5% (426/564)
Hizb 60 52.1% (150/288)

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيْتُونِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.

وَطُورِ سِينِينَ ﴿٢﴾

Da Dũr Sĩnĩna.

وَهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ٱلْأَمِينِ ﴿٣﴾

Da wannan gari amintacce.

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِىٓ أَحْسَنِ تَقْوِيمٍۢ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.

ثُمَّ رَدَدْنَـٰهُ أَسْفَلَ سَـٰفِلِينَ ﴿٥﴾

Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۢ ﴿٦﴾

Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِٱلدِّينِ ﴿٧﴾

To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?

أَلَيْسَ ٱللَّهُ بِأَحْكَمِ ٱلْحَـٰكِمِينَ ﴿٨﴾

Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?

ٱقْرَأْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلَّذِى خَلَقَ ﴿١﴾

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِنْ عَلَقٍ ﴿٢﴾

Ya hahitta mutum daga gudan jini.

ٱقْرَأْ وَرَبُّكَ ٱلْأَكْرَمُ ﴿٣﴾

Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.

ٱلَّذِى عَلَّمَ بِٱلْقَلَمِ ﴿٤﴾

Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

عَلَّمَ ٱلْإِنسَـٰنَ مَا لَمْ يَعْلَمْ ﴿٥﴾

Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

كَلَّآ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لَيَطْغَىٰٓ ﴿٦﴾

A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

أَن رَّءَاهُ ٱسْتَغْنَىٰٓ ﴿٧﴾

Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجْعَىٰٓ ﴿٨﴾

Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يَنْهَىٰ ﴿٩﴾

Shin, kã ga wanda ke hana.

عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰٓ ﴿١٠﴾

Bãwã idan yã yi salla?

أَرَءَيْتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلْهُدَىٰٓ ﴿١١﴾

Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

أَوْ أَمَرَ بِٱلتَّقْوَىٰٓ ﴿١٢﴾

Ko ya yi umurni da taƙawa?

أَرَءَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ ﴿١٣﴾

Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ ﴿١٤﴾

Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًۢا بِٱلنَّاصِيَةِ ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

نَاصِيَةٍۢ كَـٰذِبَةٍ خَاطِئَةٍۢ ﴿١٦﴾

Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

فَلْيَدْعُ نَادِيَهُۥ ﴿١٧﴾

Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

سَنَدْعُ ٱلزَّبَانِيَةَ ﴿١٨﴾

Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَٱسْجُدْ وَٱقْتَرِب ۩ ﴿١٩﴾

A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).

Shafi 598
Hizb 60
سورة القدر
Juz 30 80.3% (453/564)
Hizb 60 61.5% (177/288)

إِنَّآ أَنزَلْنَـٰهُ فِى لَيْلَةِ ٱلْقَدْرِ ﴿١﴾

Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi (Alƙur'ãni) a cikin Lailatul ƙadari (daren daraja)

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا لَيْلَةُ ٱلْقَدْرِ ﴿٢﴾

To, me ya sanar da kai abin da ake cewa Lailatul ¡adari?

لَيْلَةُ ٱلْقَدْرِ خَيْرٌۭ مِّنْ أَلْفِ شَهْرٍۢ ﴿٣﴾

Lailatul ¡adari mafi alheri ne daga wasu watanni dubu.

تَنَزَّلُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ فِيهَا بِإِذْنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمْرٍۢ ﴿٤﴾

Mala'iku da Rũhi suna sauka a cikinsa da iznin Ubangijinsu sabõda kowane umurni.

سَلَـٰمٌ هِىَ حَتَّىٰ مَطْلَعِ ٱلْفَجْرِ ﴿٥﴾

Sallama ne shi daren, har fitar alfijiri.

لَمْ يَكُنِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ مِنْ أَهْلِ ٱلْكِتَـٰبِ وَٱلْمُشْرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّىٰ تَأْتِيَهُمُ ٱلْبَيِّنَةُ ﴿١﴾

Waɗanda suka kãfirta daga mũtanen Littafi, da mushirikai, ba su kasance masu gushewa daga gaskiya ba har hujja ta je musu.

رَسُولٌۭ مِّنَ ٱللَّهِ يَتْلُوا۟ صُحُفًۭا مُّطَهَّرَةًۭ ﴿٢﴾

Wani Manzo daga Allah, yana karatun wasu takardu masu tsarki.

فِيهَا كُتُبٌۭ قَيِّمَةٌۭ ﴿٣﴾

A cikinsu akwai wasu littafai mãsu ƙĩma da daraja.

وَمَا تَفَرَّقَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ إِلَّا مِنۢ بَعْدِ مَا جَآءَتْهُمُ ٱلْبَيِّنَةُ ﴿٤﴾

Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su sãɓa wa juna ba face bayan hujjar ta je musu.

وَمَآ أُمِرُوٓا۟ إِلَّا لِيَعْبُدُوا۟ ٱللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُوا۟ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤْتُوا۟ ٱلزَّكَوٰةَ ۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلْقَيِّمَةِ ﴿٥﴾

Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah suna mãsu tsarkake addinin gare Shi, mãsu karkata zuwa ga addinin gaskiya, kuma su tsai da salla kuma su bãyar da zakka, kuma wannan shi ne addinin waɗanda suke a kan hanyar ƙwarai.

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ مِنْ أَهْلِ ٱلْكِتَـٰبِ وَٱلْمُشْرِكِينَ فِى نَارِ جَهَنَّمَ خَـٰلِدِينَ فِيهَآ ۚ أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمْ شَرُّ ٱلْبَرِيَّةِ ﴿٦﴾

Lalle ne waɗanda suka kafirta daga mutanen Littafi da mushirikai sana cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waɗannan su ne mafi ashararancin tãlikai.

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمْ خَيْرُ ٱلْبَرِيَّةِ ﴿٧﴾

Lalle ne waɗanda suka yi ĩmani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan su ne mafifita alherin halitta.

Shafi 599
Hizb 60
سورة البينة
Juz 30 82.4% (465/564)
Hizb 60 65.6% (189/288)

جَزَآؤُهُمْ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّـٰتُ عَدْنٍۢ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَـٰرُ خَـٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًۭا ۖ رَّضِىَ ٱللَّهُ عَنْهُمْ وَرَضُوا۟ عَنْهُ ۚ ذَٰلِكَ لِمَنْ خَشِىَ رَبَّهُۥ ﴿٨﴾

Sakamakonsu, a wurin Ubangijinsu, shi ne gidajen Aljannar zama, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu sunã madawwama a cikinta har abada. Allah Ya yarda da su, kuma su, sun yarda da Shi. wannan sakamako ne ga wanda ya ji tsõron Ubangijinsa.

إِذَا زُلْزِلَتِ ٱلْأَرْضُ زِلْزَالَهَا ﴿١﴾

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

وَأَخْرَجَتِ ٱلْأَرْضُ أَثْقَالَهَا ﴿٢﴾

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

وَقَالَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا لَهَا ﴿٣﴾

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

يَوْمَئِذٍۢ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا ﴿٤﴾

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا ﴿٥﴾

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

يَوْمَئِذٍۢ يَصْدُرُ ٱلنَّاسُ أَشْتَاتًۭا لِّيُرَوْا۟ أَعْمَـٰلَهُمْ ﴿٦﴾

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًۭا يَرَهُۥ ﴿٧﴾

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍۢ شَرًّۭا يَرَهُۥ ﴿٨﴾

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.

وَٱلْعَـٰدِيَـٰتِ ضَبْحًۭا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.

فَٱلْمُورِيَـٰتِ قَدْحًۭا ﴿٢﴾

Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.

فَٱلْمُغِيرَٰتِ صُبْحًۭا ﴿٣﴾

Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.

فَأَثَرْنَ بِهِۦ نَقْعًۭا ﴿٤﴾

Sai su motsar da ƙũra game da shi.

فَوَسَطْنَ بِهِۦ جَمْعًا ﴿٥﴾

Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.

إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٌۭ ﴿٦﴾

Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.

وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٌۭ ﴿٧﴾

Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka.

وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلْخَيْرِ لَشَدِيدٌ ﴿٨﴾

Kuma 1alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.

۞ أَفَلَا يَعْلَمُ إِذَا بُعْثِرَ مَا فِى ٱلْقُبُورِ ﴿٩﴾

Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.

Shafi 600
Hizb 60
سورة العاديات
Juz 30 85.6% (483/564)
Hizb 60 71.9% (207/288)

وَحُصِّلَ مَا فِى ٱلصُّدُورِ ﴿١٠﴾

Aka bayyana abin da ke cikin zukata.

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمْ يَوْمَئِذٍۢ لَّخَبِيرٌۢ ﴿١١﴾

Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne?

ٱلْقَارِعَةُ ﴿١﴾

Mai ƙwanƙwasar (zukata da tsõro)!

مَا ٱلْقَارِعَةُ ﴿٢﴾

Mẽnẽ ne mai ƙwanƙwasa?

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْقَارِعَةُ ﴿٣﴾

Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa mai ƙwanƙwasa?

يَوْمَ يَكُونُ ٱلنَّاسُ كَٱلْفَرَاشِ ٱلْمَبْثُوثِ ﴿٤﴾

Rãnar da mutãne za su kasance kamar 'ya'yan fari mãsu wãtsuwa.

وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ ٱلْمَنفُوشِ ﴿٥﴾

Kuma duwãtsu su kasance kamar gãshin sũfin da aka saɓe.

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتْ مَوَٰزِينُهُۥ ﴿٦﴾

To, amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi.

فَهُوَ فِى عِيشَةٍۢ رَّاضِيَةٍۢ ﴿٧﴾

To, shi yana a cikin wata rayuwa yardadda.

وَأَمَّا مَنْ خَفَّتْ مَوَٰزِينُهُۥ ﴿٨﴾

Kuma amma wanda ma'aunansa suka yi sauƙi (bãbu nauyi).

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٌۭ ﴿٩﴾

To, uwarsa Hãwiya ce.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا هِيَهْ ﴿١٠﴾

Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?

نَارٌ حَامِيَةٌۢ ﴿١١﴾

Wata wuta ce mai zafi.

أَلْهَىٰكُمُ ٱلتَّكَاثُرُ ﴿١﴾

Alfahari da yawan dũkiya da dangi ya shagaltar da ku (dagaibada mai amfaninku).

حَتَّىٰ زُرْتُمُ ٱلْمَقَابِرَ ﴿٢﴾

Har kuka ziyarci kaburbura.

كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ ﴿٣﴾

A'aha! (Nan gaba) zã ku sani.

ثُمَّ كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ ﴿٤﴾

Sa'an nan, tabbas, zã ku sani.

كَلَّا لَوْ تَعْلَمُونَ عِلْمَ ٱلْيَقِينِ ﴿٥﴾

Haƙĩƙa, da kuna da sani sani na yaƙĩni.

لَتَرَوُنَّ ٱلْجَحِيمَ ﴿٦﴾

Lalle ne da kuna ganin Jahĩm.

ثُمَّ لَتَرَوُنَّهَا عَيْنَ ٱلْيَقِينِ ﴿٧﴾

Sa'an nan lalle ne za ku gan ta, da idanu, bayyane.

ثُمَّ لَتُسْـَٔلُنَّ يَوْمَئِذٍ عَنِ ٱلنَّعِيمِ ﴿٨﴾

Sa'an nan lalle ne za a tambaye ku, a rãnar nan lãbãrin ni'imar (da aka yi muku).

Shafi 601
Hizb 60
سورة العصر
Juz 30 89.4% (504/564)
Hizb 60 79.2% (228/288)

وَٱلْعَصْرِ ﴿١﴾

Ina rantsuwa da zãmani.

إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لَفِى خُسْرٍ ﴿٢﴾

Lalle ne mutum yana a cikin hasara.

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْحَقِّ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ ﴿٣﴾

Fãce waɗanda suka yi ĩmani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi wa juna wasiyya da bin gaskiya, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin haƙuri (su kam, basu cikin hasara).

وَيْلٌۭ لِّكُلِّ هُمَزَةٍۢ لُّمَزَةٍ ﴿١﴾

Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa).

ٱلَّذِى جَمَعَ مَالًۭا وَعَدَّدَهُۥ ﴿٢﴾

Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa.

يَحْسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخْلَدَهُۥ ﴿٣﴾

Yana zaton cẽwa dũkiyarsa za ta dawwamar da shi.

كَلَّا ۖ لَيُنۢبَذَنَّ فِى ٱلْحُطَمَةِ ﴿٤﴾

A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحُطَمَةُ ﴿٥﴾

Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa Huɗama?

نَارُ ٱللَّهِ ٱلْمُوقَدَةُ ﴿٦﴾

Wutar Allah ce wadda ake hurawa.

ٱلَّتِى تَطَّلِعُ عَلَى ٱلْأَفْـِٔدَةِ ﴿٧﴾

Wadda take lẽƙãwa a kan zukata.

إِنَّهَا عَلَيْهِم مُّؤْصَدَةٌۭ ﴿٨﴾

Lalle ne ita abar kullẽwa cea kansu.

فِى عَمَدٍۢ مُّمَدَّدَةٍۭ ﴿٩﴾

A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu.

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصْحَـٰبِ ٱلْفِيلِ ﴿١﴾

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?

أَلَمْ يَجْعَلْ كَيْدَهُمْ فِى تَضْلِيلٍۢ ﴿٢﴾

Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?

وَأَرْسَلَ عَلَيْهِمْ طَيْرًا أَبَابِيلَ ﴿٣﴾

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.

تَرْمِيهِم بِحِجَارَةٍۢ مِّن سِجِّيلٍۢ ﴿٤﴾

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.

فَجَعَلَهُمْ كَعَصْفٍۢ مَّأْكُولٍۭ ﴿٥﴾

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?

Shafi 602
Hizb 60
سورة قريش
Juz 30 92.4% (521/564)
Hizb 60 85.1% (245/288)

لِإِيلَـٰفِ قُرَيْشٍ ﴿١﴾

Sabõda sãbon ¡uraishawa.

إِۦلَـٰفِهِمْ رِحْلَةَ ٱلشِّتَآءِ وَٱلصَّيْفِ ﴿٢﴾

Sãbonsu na tafiyar hunturu da ta bazara.

فَلْيَعْبُدُوا۟ رَبَّ هَـٰذَا ٱلْبَيْتِ ﴿٣﴾

Sabõda haka sai su bauta wa Ubangijin wannan Gida (Ka'abah).

ٱلَّذِىٓ أَطْعَمَهُم مِّن جُوعٍۢ وَءَامَنَهُم مِّنْ خَوْفٍۭ ﴿٤﴾

wanda Ya ciyar da su (Ya hana su) daga yunwa, kuma Ya amintar da su daga wani tsõro.

أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يُكَذِّبُ بِٱلدِّينِ ﴿١﴾

Shin, ka ga wanda ke ƙaryatãwa game da sakamako?

فَذَٰلِكَ ٱلَّذِى يَدُعُّ ٱلْيَتِيمَ ﴿٢﴾

To, wannan shi ne ke tunkue marãya (daga haƙƙinsa).

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ ﴿٣﴾

Kuma bã ya kwaaitarwa bisa bãyar da abinci ga matalauci.

فَوَيْلٌۭ لِّلْمُصَلِّينَ ﴿٤﴾

To, bone yã tabbata ga masallata.

ٱلَّذِينَ هُمْ عَن صَلَاتِهِمْ سَاهُونَ ﴿٥﴾

Waɗanda suke masu shagala daga sallarsu.

ٱلَّذِينَ هُمْ يُرَآءُونَ ﴿٦﴾

Waɗanda suke yin riya (ga ayyukansu)

وَيَمْنَعُونَ ٱلْمَاعُونَ ﴿٧﴾

Kuma suna hana taimako.

إِنَّآ أَعْطَيْنَـٰكَ ٱلْكَوْثَرَ ﴿١﴾

Lalle ne Mu, Mun yi maka kyauta mai yawa.

فَصَلِّ لِرَبِّكَ وَٱنْحَرْ ﴿٢﴾

Saboda haka, ka yi salla dõmin Ubangijinka, kuma ka sõke (baiko, wato sukar raƙumi).

إِنَّ شَانِئَكَ هُوَ ٱلْأَبْتَرُ ﴿٣﴾

Lalle mai aibanta ka shi ne mai yankakkiyar albarka.

Shafi 603
Hizb 60
سورة الكافرون
Juz 30 94.9% (535/564)
Hizb 60 89.9% (259/288)

قُلْ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْكَـٰفِرُونَ ﴿١﴾

Ka ce: "Ya kũ kãfirai!"

لَآ أَعْبُدُ مَا تَعْبُدُونَ ﴿٢﴾

"Bã zan bautã wa abin da kuke bautã wa ba."

وَلَآ أَنتُمْ عَـٰبِدُونَ مَآ أَعْبُدُ ﴿٣﴾

"Kuma kũ, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bautã wa ba."

وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٌۭ مَّا عَبَدتُّمْ ﴿٤﴾

"Kuma nĩ ban zama mai bautã wa abin da kuka bautã wa ba."

وَلَآ أَنتُمْ عَـٰبِدُونَ مَآ أَعْبُدُ ﴿٥﴾

"Kuma kũ, ba ku zama mãsu bautã wa abin da nake bautã wa ba."

لَكُمْ دِينُكُمْ وَلِىَ دِينِ ﴿٦﴾

"Addininku na garẽ ku, kuma addinina yanã gare ni."

إِذَا جَآءَ نَصْرُ ٱللَّهِ وَٱلْفَتْحُ ﴿١﴾

Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara.

وَرَأَيْتَ ٱلنَّاسَ يَدْخُلُونَ فِى دِينِ ٱللَّهِ أَفْوَاجًۭا ﴿٢﴾

Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya.

فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَٱسْتَغْفِرْهُ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابًۢا ﴿٣﴾

To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne.

تَبَّتْ يَدَآ أَبِى لَهَبٍۢ وَتَبَّ ﴿١﴾

Hannãye biyu na Abũlahabi sun halaka, kuma ya halaka.

مَآ أَغْنَىٰ عَنْهُ مَالُهُۥ وَمَا كَسَبَ ﴿٢﴾

Dũkiyarsa ba ta tsare masa kõme ba, da abin da ya tãra.

سَيَصْلَىٰ نَارًۭا ذَاتَ لَهَبٍۢ ﴿٣﴾

Zã ya shiga wuta mai hũruwa.

وَٱمْرَأَتُهُۥ حَمَّالَةَ ٱلْحَطَبِ ﴿٤﴾

Tãre da matarsa mai ɗaukar itacen (wuta).

فِى جِيدِهَا حَبْلٌۭ مِّن مَّسَدٍۭ ﴿٥﴾

A cikin kyakkyãwan wuyanta akwai igiya ta kaba (Rãnar ¡iyãma).

Shafi 604
Hizb 60
سورة الإخلاص
Juz 30 97.3% (549/564)
Hizb 60 94.8% (273/288)

قُلْ هُوَ ٱللَّهُ أَحَدٌ ﴿١﴾

Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci."

ٱللَّهُ ٱلصَّمَدُ ﴿٢﴾

"Allah wanda ake nufin Sa da buƙata."

لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ ﴿٣﴾

"Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba."

وَلَمْ يَكُن لَّهُۥ كُفُوًا أَحَدٌۢ ﴿٤﴾

"Kuma babu ɗaya da ya kasance tamka a gare Shi."

قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلْفَلَقِ ﴿١﴾

Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya"

مِن شَرِّ مَا خَلَقَ ﴿٢﴾

"Daga sharrin abin da Ya halitta."

وَمِن شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ ﴿٣﴾

"Da sharrin dare, idan ya yi duhu."

وَمِن شَرِّ ٱلنَّفَّـٰثَـٰتِ فِى ٱلْعُقَدِ ﴿٤﴾

"Da sharrin mãtã mãsu tõfi a cikin ƙulle-ƙulle."

وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ ﴿٥﴾

"Da sharrin mai hãsada idan ya yi hasada."

قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلنَّاسِ ﴿١﴾

Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne."

مَلِكِ ٱلنَّاسِ ﴿٢﴾

"Mamallakin mutane."

إِلَـٰهِ ٱلنَّاسِ ﴿٣﴾

"Abin bautãwar mutãne."

مِن شَرِّ ٱلْوَسْوَاسِ ٱلْخَنَّاسِ ﴿٤﴾

"Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa."

ٱلَّذِى يُوَسْوِسُ فِى صُدُورِ ٱلنَّاسِ ﴿٥﴾

"Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane."

مِنَ ٱلْجِنَّةِ وَٱلنَّاسِ ﴿٦﴾

"Daga aljannu da mutane."

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
أستغفر الله Ina neman gafara daga Allah