النبإ · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Hizb 59 na Alkur'ani

Hizb 59 wani ɓangare ne na Juz 30. Yana ɗauke da ayoyi 276 a shafi(shafuffuka) 23 na Mushaf.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Shafi 582
Hizb 59
سورة النبإ
Juz 30 0.0% (0/564)
Hizb 59 0.0% (0/276)

عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ ﴿١﴾

A kan mẽ suke tambayar jũna?

عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلْعَظِيمِ ﴿٢﴾

A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

ٱلَّذِى هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ ﴿٣﴾

Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

كَلَّا سَيَعْلَمُونَ ﴿٤﴾

A'aha! Zã su sani.

ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ ﴿٥﴾

Kuma, a'aha! Zã su sani.

أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ مِهَـٰدًۭا ﴿٦﴾

Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

وَٱلْجِبَالَ أَوْتَادًۭا ﴿٧﴾

Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

وَخَلَقْنَـٰكُمْ أَزْوَٰجًۭا ﴿٨﴾

Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًۭا ﴿٩﴾

Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

وَجَعَلْنَا ٱلَّيْلَ لِبَاسًۭا ﴿١٠﴾

Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

وَجَعَلْنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشًۭا ﴿١١﴾

Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًۭا شِدَادًۭا ﴿١٢﴾

Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

وَجَعَلْنَا سِرَاجًۭا وَهَّاجًۭا ﴿١٣﴾

Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

وَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلْمُعْصِرَٰتِ مَآءًۭ ثَجَّاجًۭا ﴿١٤﴾

Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

لِّنُخْرِجَ بِهِۦ حَبًّۭا وَنَبَاتًۭا ﴿١٥﴾

Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

وَجَنَّـٰتٍ أَلْفَافًا ﴿١٦﴾

Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ كَانَ مِيقَـٰتًۭا ﴿١٧﴾

Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

يَوْمَ يُنفَخُ فِى ٱلصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًۭا ﴿١٨﴾

Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ أَبْوَٰبًۭا ﴿١٩﴾

Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

وَسُيِّرَتِ ٱلْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا ﴿٢٠﴾

Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًۭا ﴿٢١﴾

Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

لِّلطَّـٰغِينَ مَـَٔابًۭا ﴿٢٢﴾

Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

لَّـٰبِثِينَ فِيهَآ أَحْقَابًۭا ﴿٢٣﴾

Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًۭا وَلَا شَرَابًا ﴿٢٤﴾

Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

إِلَّا حَمِيمًۭا وَغَسَّاقًۭا ﴿٢٥﴾

Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

جَزَآءًۭ وِفَاقًا ﴿٢٦﴾

Sakamako mai dãcẽwa.

إِنَّهُمْ كَانُوا۟ لَا يَرْجُونَ حِسَابًۭا ﴿٢٧﴾

Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا كِذَّابًۭا ﴿٢٨﴾

Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

وَكُلَّ شَىْءٍ أَحْصَيْنَـٰهُ كِتَـٰبًۭا ﴿٢٩﴾

Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

فَذُوقُوا۟ فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا ﴿٣٠﴾

Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

Shafi 583
Hizb 59
سورة النبإ
Juz 30 5.3% (30/564)
Hizb 59 10.9% (30/276)

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا ﴿٣١﴾

Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

حَدَآئِقَ وَأَعْنَـٰبًۭا ﴿٣٢﴾

Lambuna da inabõbi.

وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًۭا ﴿٣٣﴾

Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

وَكَأْسًۭا دِهَاقًۭا ﴿٣٤﴾

Da hinjãlan giya cikakku.

لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا كِذَّٰبًۭا ﴿٣٥﴾

Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

جَزَآءًۭ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًۭا ﴿٣٦﴾

Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

رَّبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَـٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًۭا ﴿٣٧﴾

Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ صَفًّۭا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَـٰنُ وَقَالَ صَوَابًۭا ﴿٣٨﴾

Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا ﴿٣٩﴾

Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

إِنَّآ أَنذَرْنَـٰكُمْ عَذَابًۭا قَرِيبًۭا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَـٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا ﴿٤٠﴾

Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"

وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًۭا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًۭا ﴿٢﴾

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًۭا ﴿٣﴾

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًۭا ﴿٤﴾

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا ﴿٥﴾

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ ﴿٦﴾

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ ﴿٧﴾

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ ﴿٨﴾

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌۭ ﴿٩﴾

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ ﴿١٠﴾

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًۭا نَّخِرَةًۭ ﴿١١﴾

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ ﴿١٢﴾

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ ﴿١٣﴾

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ ﴿١٤﴾

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ ﴿١٥﴾

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

Shafi 584
Hizb 59
سورة النازعات
Juz 30 9.8% (55/564)
Hizb 59 19.9% (55/276)

إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى ﴿١٦﴾

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿١٧﴾

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ﴿١٩﴾

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٢٠﴾

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﴿٢١﴾

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﴿٢٣﴾

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٤﴾

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ ﴿٢٥﴾

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ ﴿٢٦﴾

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا ﴿٢٧﴾

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا ﴿٢٨﴾

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا ﴿٢٩﴾

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ ﴿٣٠﴾

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا ﴿٣١﴾

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا ﴿٣٢﴾

Da duwatsu, Yã kafe ta.

مَتَـٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ ﴿٣٣﴾

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٣٤﴾

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ ﴿٣٥﴾

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ ﴿٣٦﴾

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ﴿٣٧﴾

To, amma wanda ya yi girman kai.

وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا ﴿٣٨﴾

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ ﴿٣٩﴾

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ ﴿٤٠﴾

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ ﴿٤١﴾

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا ﴿٤٢﴾

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ ﴿٤٣﴾

Me ya haɗã ka da ambatonta?

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ ﴿٤٤﴾

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا ﴿٤٥﴾

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا ﴿٤٦﴾

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.

Shafi 585
Hizb 59
سورة عبس
Juz 30 15.2% (86/564)
Hizb 59 31.2% (86/276)

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ ﴿١﴾

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ ﴿٢﴾

Sabõda makãho yã je masa.

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ ﴿٣﴾

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ ﴿٤﴾

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ ﴿٥﴾

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ ﴿٦﴾

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ ﴿٧﴾

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ ﴿٨﴾

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

وَهُوَ يَخْشَىٰ ﴿٩﴾

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ ﴿١٠﴾

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌۭ ﴿١١﴾

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ ﴿١٢﴾

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

فِى صُحُفٍۢ مُّكَرَّمَةٍۢ ﴿١٣﴾

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

مَّرْفُوعَةٍۢ مُّطَهَّرَةٍۭ ﴿١٤﴾

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

بِأَيْدِى سَفَرَةٍۢ ﴿١٥﴾

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

كِرَامٍۭ بَرَرَةٍۢ ﴿١٦﴾

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

قُتِلَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ ﴿١٧﴾

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ ﴿١٨﴾

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ ﴿١٩﴾

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ ﴿٢٠﴾

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ ﴿٢١﴾

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ ﴿٢٣﴾

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ ﴿٢٤﴾

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّۭا ﴿٢٥﴾

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّۭا ﴿٢٦﴾

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّۭا ﴿٢٧﴾

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

وَعِنَبًۭا وَقَضْبًۭا ﴿٢٨﴾

Da inabi da ciyãwa.

وَزَيْتُونًۭا وَنَخْلًۭا ﴿٢٩﴾

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

وَحَدَآئِقَ غُلْبًۭا ﴿٣٠﴾

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

وَفَـٰكِهَةًۭ وَأَبًّۭا ﴿٣١﴾

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

مَّتَـٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ ﴿٣٢﴾

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ ﴿٣٣﴾

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ ﴿٣٤﴾

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ ﴿٣٥﴾

Da uwarsa da ubansa.

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ ﴿٣٦﴾

Da mãtarsa da ɗiyansa.

لِكُلِّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍۢ شَأْنٌۭ يُغْنِيهِ ﴿٣٧﴾

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ مُّسْفِرَةٌۭ ﴿٣٨﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

ضَاحِكَةٌۭ مُّسْتَبْشِرَةٌۭ ﴿٣٩﴾

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌۭ ﴿٤٠﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ ﴿٤١﴾

Baƙi zai rufe su.

أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ ﴿٤٢﴾

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

Shafi 586
Hizb 59
سورة التكوير
Juz 30 22.7% (128/564)
Hizb 59 46.4% (128/276)

إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ ﴿١﴾

Idan rãna aka shafe haskenta

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ ﴿٣﴾

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ ﴿٤﴾

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ ﴿٥﴾

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ ﴿٦﴾

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ ﴿٧﴾

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ ﴿٨﴾

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

بِأَىِّ ذَنۢبٍۢ قُتِلَتْ ﴿٩﴾

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ ﴿١٠﴾

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ ﴿١١﴾

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ ﴿١٢﴾

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ ﴿١٣﴾

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّآ أَحْضَرَتْ ﴿١٤﴾

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ ﴿١٥﴾

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ ﴿١٦﴾

Mãsu gudu suna ɓũya.

وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ ﴿١٧﴾

Da dare idan ya bãyar da bãya.

وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ ﴿١٨﴾

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ ﴿١٩﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍۢ ﴿٢٠﴾

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

مُّطَاعٍۢ ثَمَّ أَمِينٍۢ ﴿٢١﴾

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍۢ ﴿٢٢﴾

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ ﴿٢٣﴾

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍۢ ﴿٢٤﴾

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍۢ رَّجِيمٍۢ ﴿٢٥﴾

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ ﴿٢٦﴾

Shin, a inã zã ku tafi?

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَـٰلَمِينَ ﴿٢٧﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ ﴿٢٨﴾

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٢٩﴾

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

Shafi 587
Hizb 59
سورة الإنفطار
Juz 30 27.8% (157/564)
Hizb 59 56.9% (157/276)

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتْ ﴿١﴾

Idan sama ta tsãge.

وَإِذَا ٱلْكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتْ ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka wãtse.

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ فُجِّرَتْ ﴿٣﴾

Kuma idan tẽkuna aka facce su.

وَإِذَا ٱلْقُبُورُ بُعْثِرَتْ ﴿٤﴾

Kuma idan kaburbura aka tõne su.

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ ﴿٥﴾

Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلْكَرِيمِ ﴿٦﴾

Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

ٱلَّذِى خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ ﴿٧﴾

Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.

فِىٓ أَىِّ صُورَةٍۢ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ ﴿٨﴾

A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.

كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ ﴿٩﴾

A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!

وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَـٰفِظِينَ ﴿١٠﴾

Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.

كِرَامًۭا كَـٰتِبِينَ ﴿١١﴾

Mãsu daraja, marubũta.

يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ ﴿١٢﴾

Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.

إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍۢ ﴿١٣﴾

Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.

وَإِنَّ ٱلْفُجَّارَ لَفِى جَحِيمٍۢ ﴿١٤﴾

Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.

يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ ٱلدِّينِ ﴿١٥﴾

Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.

وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَآئِبِينَ ﴿١٦﴾

Bã zã su faku daga gare ta ba.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ ﴿١٧﴾

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?

ثُمَّ مَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ ﴿١٨﴾

Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?

يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌۭ لِّنَفْسٍۢ شَيْـًۭٔا ۖ وَٱلْأَمْرُ يَوْمَئِذٍۢ لِّلَّهِ ﴿١٩﴾

Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.

وَيْلٌۭ لِّلْمُطَفِّفِينَ ﴿١﴾

Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.

ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكْتَالُوا۟ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسْتَوْفُونَ ﴿٢﴾

Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.

وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ ﴿٣﴾

Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa

أَلَا يَظُنُّ أُو۟لَـٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ ﴿٤﴾

Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?

لِيَوْمٍ عَظِيمٍۢ ﴿٥﴾

Domin yini mai girma.

يَوْمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٦﴾

Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?

Shafi 588
Hizb 59
سورة المطففين
Juz 30 32.3% (182/564)
Hizb 59 65.9% (182/276)

كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْفُجَّارِ لَفِى سِجِّينٍۢ ﴿٧﴾

Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سِجِّينٌۭ ﴿٨﴾

Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?

كِتَـٰبٌۭ مَّرْقُومٌۭ ﴿٩﴾

Wani 1ittãfi ne rubũtacce.

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ ﴿١٠﴾

Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿١١﴾

Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.

وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ ﴿١٢﴾

Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿١٣﴾

Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.

كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ ﴿١٤﴾

A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.

كَلَّآ إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍۢ لَّمَحْجُوبُونَ ﴿١٥﴾

A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.

ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا۟ ٱلْجَحِيمِ ﴿١٦﴾

Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.

ثُمَّ يُقَالُ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ ﴿١٧﴾

Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."

كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْأَبْرَارِ لَفِى عِلِّيِّينَ ﴿١٨﴾

A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ ﴿١٩﴾

Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?

كِتَـٰبٌۭ مَّرْقُومٌۭ ﴿٢٠﴾

Wani littãfi ne rubũtacce.

يَشْهَدُهُ ٱلْمُقَرَّبُونَ ﴿٢١﴾

Muƙarrabai suke halarta shi.

إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ ﴿٢٢﴾

Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.

عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ ﴿٢٣﴾

A kan karagu, suna ta kallo.

تَعْرِفُ فِى وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ ٱلنَّعِيمِ ﴿٢٤﴾

Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.

يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍۢ مَّخْتُومٍ ﴿٢٥﴾

Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.

خِتَـٰمُهُۥ مِسْكٌۭ ۚ وَفِى ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ ٱلْمُتَنَـٰفِسُونَ ﴿٢٦﴾

¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.

وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسْنِيمٍ ﴿٢٧﴾

Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.

عَيْنًۭا يَشْرَبُ بِهَا ٱلْمُقَرَّبُونَ ﴿٢٨﴾

(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.

إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجْرَمُوا۟ كَانُوا۟ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ يَضْحَكُونَ ﴿٢٩﴾

Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.

وَإِذَا مَرُّوا۟ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ ﴿٣٠﴾

Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.

وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓا۟ إِلَىٰٓ أَهْلِهِمُ ٱنقَلَبُوا۟ فَكِهِينَ ﴿٣١﴾

Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.

وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ ﴿٣٢﴾

Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."

وَمَآ أُرْسِلُوا۟ عَلَيْهِمْ حَـٰفِظِينَ ﴿٣٣﴾

Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.

فَٱلْيَوْمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنَ ٱلْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ ﴿٣٤﴾

To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.

Shafi 589
Hizb 59
سورة المطففين
Juz 30 37.2% (210/564)
Hizb 59 76.1% (210/276)

عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ ﴿٣٥﴾

A kan karagu, suna ta kallo.

هَلْ ثُوِّبَ ٱلْكُفَّارُ مَا كَانُوا۟ يَفْعَلُونَ ﴿٣٦﴾

Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa?

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ ﴿١﴾

Idan sama ta kẽce,

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ ﴿٢﴾

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ ﴿٣﴾

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ ﴿٤﴾

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ ﴿٥﴾

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًۭا فَمُلَـٰقِيهِ ﴿٦﴾

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ ﴿٧﴾

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًۭا يَسِيرًۭا ﴿٨﴾

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًۭا ﴿٩﴾

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ ﴿١٠﴾

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًۭا ﴿١١﴾

To, zã shi dinga kiran halaka!

وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا ﴿١٢﴾

Kuma ya shiga sa'ĩr.

إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا ﴿١٣﴾

Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ ﴿١٤﴾

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًۭا ﴿١٥﴾

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ ﴿١٦﴾

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ ﴿١٧﴾

Da dare, da abin da ya ƙunsa.

وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ ﴿١٨﴾

Da watã idan (haskensa) ya cika.

لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍۢ ﴿١٩﴾

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ ﴿٢٠﴾

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩ ﴿٢١﴾

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ ﴿٢٢﴾

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ ﴿٢٣﴾

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ ﴿٢٤﴾

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ ﴿٢٥﴾

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.

Shafi 590
Hizb 59
سورة البروج
Juz 30 42.0% (237/564)
Hizb 59 85.9% (237/276)

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْبُرُوجِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara.

وَٱلْيَوْمِ ٱلْمَوْعُودِ ﴿٢﴾

Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa,

وَشَاهِدٍۢ وَمَشْهُودٍۢ ﴿٣﴾

Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa

قُتِلَ أَصْحَـٰبُ ٱلْأُخْدُودِ ﴿٤﴾

An la'ani mutãnen rãmi.

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلْوَقُودِ ﴿٥﴾

Wato wuta wadda aka hura.

إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌۭ ﴿٦﴾

A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune.

وَهُمْ عَلَىٰ مَا يَفْعَلُونَ بِٱلْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌۭ ﴿٧﴾

Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce.

وَمَا نَقَمُوا۟ مِنْهُمْ إِلَّآ أَن يُؤْمِنُوا۟ بِٱللَّهِ ٱلْعَزِيزِ ٱلْحَمِيدِ ﴿٨﴾

Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa.

ٱلَّذِى لَهُۥ مُلْكُ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَىْءٍۢ شَهِيدٌ ﴿٩﴾

Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake.

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُوا۟ ٱلْمُؤْمِنِينَ وَٱلْمُؤْمِنَـٰتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا۟ فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ ٱلْحَرِيقِ ﴿١٠﴾

Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara.

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ جَنَّـٰتٌۭ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَـٰرُ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْفَوْزُ ٱلْكَبِيرُ ﴿١١﴾

Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba.

إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ ﴿١٢﴾

Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai.

إِنَّهُۥ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ ﴿١٣﴾

Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa).

وَهُوَ ٱلْغَفُورُ ٱلْوَدُودُ ﴿١٤﴾

Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya.

ذُو ٱلْعَرْشِ ٱلْمَجِيدُ ﴿١٥﴾

Mai Al'arshi mai girma

فَعَّالٌۭ لِّمَا يُرِيدُ ﴿١٦﴾

Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi.

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْجُنُودِ ﴿١٧﴾

Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka.

فِرْعَوْنَ وَثَمُودَ ﴿١٨﴾

Fir'auna da samũdãwa?

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ فِى تَكْذِيبٍۢ ﴿١٩﴾

Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa.

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطٌۢ ﴿٢٠﴾

Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa).

بَلْ هُوَ قُرْءَانٌۭ مَّجِيدٌۭ ﴿٢١﴾

Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma.

فِى لَوْحٍۢ مَّحْفُوظٍۭ ﴿٢٢﴾

A cikin Allo tsararre.

Shafi 591
Hizb 59
سورة الطارق
Juz 30 45.9% (259/564)
Hizb 59 93.8% (259/276)

وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ ﴿٢﴾

To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?

ٱلنَّجْمُ ٱلثَّاقِبُ ﴿٣﴾

Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.

إِن كُلُّ نَفْسٍۢ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌۭ ﴿٤﴾

Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ مِمَّ خُلِقَ ﴿٥﴾

To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?

خُلِقَ مِن مَّآءٍۢ دَافِقٍۢ ﴿٦﴾

An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.

يَخْرُجُ مِنۢ بَيْنِ ٱلصُّلْبِ وَٱلتَّرَآئِبِ ﴿٧﴾

Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجْعِهِۦ لَقَادِرٌۭ ﴿٨﴾

Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.

يَوْمَ تُبْلَى ٱلسَّرَآئِرُ ﴿٩﴾

Rãnar da ake jarrabawar asirai.

فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٍۢ وَلَا نَاصِرٍۢ ﴿١٠﴾

Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجْعِ ﴿١١﴾

Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.

وَٱلْأَرْضِ ذَاتِ ٱلصَّدْعِ ﴿١٢﴾

Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,

إِنَّهُۥ لَقَوْلٌۭ فَصْلٌۭ ﴿١٣﴾

Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki

وَمَا هُوَ بِٱلْهَزْلِ ﴿١٤﴾

Kuma shĩ bã bananci bane

إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًۭا ﴿١٥﴾

Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.

وَأَكِيدُ كَيْدًۭا ﴿١٦﴾

Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.

فَمَهِّلِ ٱلْكَـٰفِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًۢا ﴿١٧﴾

Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا إله إلا الله Babu abin bautawa sai Allah